Sanata Ben bruce ya bayyana cewa idan kuna so Majalisa ta gyaru to sai kun sa ido ga yan Majalisun ku domin kuwa suna tsoronku. zaboda zaku iya hanashi zarcewa. ya nuna kada talaka ya gaza wajen sa ido domin hakan ne mafita gareshi. Kuma nuna wa talakawa idan har basu gyara kansu ba to fa baza su samu gyaran da suke bukata ba domin idan aka samu mabiya masu halin banza dole ne shugaban su ya zaman mai irin halinshu. Wannan shawara ta wannan dan majalisa nada matukar anfani domin kuwa abubuwa da dama na faruwa a majalisa kuma ya kamata musan wane yan majalisun ne basu goyon bayan ci gaban kasar nan dan ba kowannen su bane yake goyon bayan rashin gaskiya.
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya wato NEMA ta ce mutane kusan miliyan biyu ne suke zaune a sansanonin 'yan gudun hijira daban -daban a jihohin Borno da Yobe da Gombe da Taraba da Bauchi da kuma Adamawa. Jami'in NEMA mai kula da sansanin 'yan gudun hijira dake birnin Yola, Sa'ad Bello shi ne ya sanar da haka lokacin da jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya Samantha Powers ta ziyarci sansanin na Malkohi a jihar Adamawa. Ya ce akwai wasu sansanoni 32 a jihohin Borno da Yobe da kuma Adamawa wadanda mutane sama da 189,000 da suka rasa muhalinsu suke samun mafaka. Malam Bello ya ce jihar Borno tana da sansanoni 19, wadanda 'yan gudun hijira sama da 150,000 suke samun mafaka, jihar Yobe kuma tana da sansani tara inda mutane sama da 31,000 suke samun mafaka yayin da jihar Adamawa ke da sansani hudu inda mutane sama da 6,000 suke samun mafaka. Madam Samantha ta ce ta kai ziyara sansanin Malkohi ne domin ta ga yadda Amurka za ta taimakawa Najeriya waj